buhari ya maganitu kan labarin da Ake yadawa cewa bazai mikawa tinubu Mulki ba Karin dayani๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

Buhari Ya Magantu Kan Labarin Da Ake Yadawa Cewa Bazai Mikawa Tinubu Mulki Ba
25/03/2023 Nura H. Ahmad

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi watsi da rahotannin da ke cewa ba zai mika wa zababben shugaban kasa, Bola Tinubu mulki ba.

Buhari ya ce rahoton da ke ikirarin cewa ba zai mika wa Tinubu ba karya ne.


A wata sanarwa da mai magana da yawunsa Garba Shehu ya fitar, ya ce an yi duk shirye-shiryen mika mulki.


Sanarwar ta ce kwamitin mika mulki ya kunshi wakilan gwamnati da na Tinubu.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Fadar shugaban kasa na so ta yi Allah-wadai da cewa abin takaici ne kuma na karya, sannan ta yi Allah-wadai da kungiyar labaran karya da ta dangana labarin karya ga shugaban kasa Muhammadu Buhari tare da yada ta.

“Ta yaya za ku yi kamfen don neman wani, ku zabe shi sannan ku ce ba za ku mika masa ba?

Sanarwar ta ce al’ummar Daura na shirin karbar Buhari bayan ranar 29 ga watan Mayu, ya mika mulkin Najeriya ga Tinubu.

Post a Comment

Previous Post Next Post