sallah Rokon RUWA

[4/14, 9:17 AM] +234 813 420 3941: *SALLAR ROKON RUWA.*

Hikiomar sharanta ta.

 Alllah ya halicci mutum kuma ya kagi halittar sa akan yadda zai maida tamari gareshi da neman mafaka a gareshi a lokacin saukar bukatun sa. Ko lokacin da fituntunu suka kawaye shi, rokon ruwa abune wanda yake bayyane daga cikin abubuwa wadanda suke a bayyane a cikin tunanin mutum wanda Allah yasa musulmi ke maida lamarin sa gareshi don neman ruwan sama.
[4/14, 9:20 AM] +234 813 420 3941: *Ma’anar ta.*

Shi ne neman shayar wa daga Allah madaukakin sarki ga kasa da bayi, hanayar yin sallah da addu’a da kuma neman gafara.

*Hukuncinta.*

 Sallar rokon ruwa sannah ce mai karfi, Manzon Allah ﷺ‬ ya yi, kuma ya shelanta ta a cikin mutane, kuma mutane suka fito domin gabatar da sallar a filin idi sallah.

*LOKACINTA, DA KUMA SIFFARTA DA HUKUNCE-HUKUNCENTA.*

Kamar sallar idi take.

 An so limami ya sanar da yin ta kafin lokacin da wasu kwanaki.

Kuma ya jawo hankalin mutane zuwa ga tuba daga laifuffuka da kuma mayar da kayan zalunci, da kuma yin azumi da sadaka da kuma barin jiji-da-kai, domin lalle laifuka su ne sababin kawo kunci (fari), kuma kamar yin biyyaya ne shi ne sababin kawo alheri da albarka.

Post a Comment

Previous Post Next Post